Monday, February 25, 2013

BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA GWAMNA ENGR. (DR) RABI'U MUSA KWANKWASO


Ya mai girma Gwamnan jihar Kano, muna roko a gare ka da ka taimaka a sassauta dokar masu hawa babur tunda an hana goyon biyu, ya kamata a sassauta dokar daga 6pm (yamma) zuwa wani lokacin don bawa kananan yan kasuwa damar yin kasuwancin su cikin nutsuwa ba tare da fargabar komai ba. Ya mai girma wallahi kananan yan kasuwa suna cikin halin kunci akan wannan doka, sakamakon wasu masu sayan kaya sai wajen sallar la'asar suke zuwa sayan kayan saboda jihohin su da nisa, sannan ga kuma yan kasuwa da suke kasuwancin dare na kusa da gidan margayin Sheikh Nasiru Kabara da kuma yan kasuwar Dubai (Jakara), da sauran kasuwanni da dama. Ya mai girma Gwamna mafiya yawan wadannan yan kasuwa suna amfani ne da babur don gudanar da zirga zirga tsakanin wajen neman abincin su da kuma makwancin su. Fatana mai girma Gwamna ya ga wannan gajeren sako nawa, ko kuma makusanta Gwamnan su gani don isar da sakon nawa, domin a dauki matakin da ya dace. Allah ya taimaki gwamnatin jihar Kano da al'ummar jihar gaba daya, Allah ya kare mana mutuncin mu, addinin mu da al'adar mu, Ya kuma ba mu lafiya da zama lafiya.

No comments:

Post a Comment