 |
| Sir Ahmadu Bello Sardauna |
Alhaji Yusuf Tuggar, a makalar da
yake gabatarwa a duk sati a shafin BARANDAMI na jaridar RARIYA. A jaridar ta wannan mako, ya
yi wani rubutu da ya daga min hankali, marubucin ya dauko jawabin Firimiyan
Arewa, Sir Ahmadu Bello Sardauna da ya gabatar a ranar 16 ga watan Maris na
shekarar 1964, wato shekaru 50 kenan. A lokacin Sardauna ya yi shekaru biyar
biyar yana mulkar jihar Arewa. Tuggar cikin gabatar da rubutun na sa ya nemi
masu karatu su kwatanta wannan jawabi da irin siradin da muke kai a yanzu
dangane da ci gaba ta fuskar yadda shugabanninmu suke mulkarmu a yanzu. Tabbas jawabin ya sosa min
zuciya, da ba don tarihi ba, da cewa zan yi tatsuniya ce ko kuma ba a Arewar
Nijeriya hakan ya faru ba.
Ba zan cika ku da surutu ba, ga
cikakken jawabin sai ku karanta watakila kuma ku ji abin da na ji a zuciyar ta wa, sannan daga karshe sai ku yi hukunci:
“Na fara da sunan Allah, mai jinkan talikai, mai musu
rahama. Godiya ta tabatta a gare shi wanda
ya rayar da mu har muka ga karshen wannan shekara.
Mun shiga shekara ta shida a cikin mulkin kan jihar
Arewa da wani sabon tsarin mulki. Bara a cikin watan Oktoba Nijeriya ta zama
Jamhuriya a cikin tarayyan nan ta ‘Common Wealth’ wannan ko shine matakala na
karshe a cikin samowa wanan kasa cikakken iko da kuma ‘yanci na kanta.Yanzu duk
duniya tana kallon Nijeriya a kan kasa wacce take tana da cikkaken iko na
kanta, kuma bata dogara a kan ko wace kasa ba. A nan Nijeriya ta Arewa mun
karpi kowane mataki na cigaban tsarin mulkin mu a cikin farin ciki da natsuwa
wadanda suka cancanci zaman lafiyar Jihar nan da kuma fahimtar zaman duniyarta.
Ban da wannan muhimmin canjin tsari na mulki, ina
farin ciki da gani cewa mun sami matukar cigaba ta fuskan tattalin arzikin
jihar nan da kuma yaduwar ilmi. Ayyuka a kan abubuwan tsarin arzikin kasan nan
na shekaru shida suna ci gaba sosai, haka kuma ake samu a wuraren sana’o’i
wadanda ‘yan kasa da kuma mutanen waje suke kakkafawa. Na yi matukar farin ciki
da sa harsashin ginin ma’aikatar yin siminti a Sokoto kwanan nan da kuma ganin
ana kara samun ‘yan makaranta masu fita daga makarantu, tun ba ma masu fita
daga makarantun Sakandire ba wadanda suke samun muhimman ayyuka a gwamnatin
Jiha da ta tarayya ba, da ma’aikatar soja da ta ‘yan sanda, da kuma kamfanonin
ciniki da sana’o’i. A watan Nuwamba da ya wuce ne na sumu darajar da aka nada
ni shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, kuma a wanan ranar ce Jami’ar ta fara bada
digiri.
To ko wane canji da cigaba su kan kawo sababbin
wahaloli. Ko ya ya ina so in yi kokari in bayyana muku wadannan wahaloli ba
tare da wata manufa ba, kuma ba tare da wani rufe-rufe ba tun da dai kowa ya
san rufe-rufe ba hali na bane.
Nijeriya ta Arewa kasa ce wadda take da manoma, duk
galibin arzikin kasar nan ya dogara ga noma ne. Amma abin takaici shine da yawa
daga cikin samarinmu na wannan zamani sun dauka akan cewa idan suka sami ilmin
zamani, sai su gudu daga wanna al’adatamu ta gargajiya mai daraja (wato noma),
su koma su yi aiki a ofis ko a masana’anta. To, ina so in sanar da su cewa suna
yin kuskure ne.Tilas ne su fahimta cewa ba abin kunya bane ko kadan in da ko
wannenmu zai zama manomi. Ni ma kai na manomi ne. Kullum ina beken cewa dama
ayyukana za su rangwanta min da na sami lokaci na yi noma a gonata ta Bakura.
Kada ku dauka bata lokaci ne ku aika da ‘ya’yanku makarantu domin karo ilmi
idan baza su sami aikin akawu ba bayan sun gama ilimin firamare. Kowane yaro da
ya sami ilmi, zai zama ya karu da fahimtar abubuwan da duniya take ciki, zai
kuma zama dan kasa mai amfani, wanda zai taimaka wajen kara arzikin kasarsa.
Ina kara maimaita cewa arziki da ci gaban kasar nan ya dogara a kan irin
himatuwar da manomanmu suka yi ne. Ku wadanda za ku bar makarantar firamare
kwanan nan ina da wannan sako a gare ku. Ku zauna gida ku yi amfani da sabon
ilmin da kuka samu ku zama manoman bana. Idan ku da abokanku ku ka bi shawarata
kauyanku zai fi haka ci gaba, zai kuma zama wuri mai kyawun zama a cikinsa.
Muna da shirye-shirye wadanda za su ba ku sha’awa, za ku ji su kwanan nan,
wadanda kuma aka shirya musamman don a kafawa masu barin firamare guraren zama
yadda za su koyi noma a kan hanyoyin zamani, cikin tsarin jam’iyoyin tsimi da
tanadi, da kuma hanyar da za’a kara aikace-aikacen karuwar aikin gona.
Bara na tambayeku ku yi tunani a kan hanyar da za
ku bi ku taimaka wajen kara cigaban kasarku ta hanyoyi masu sauki amma fa
muhimmai, wato kamar yin ‘yan aikace-aikace wadanda za ku iya yi ta wajen
hanyar gayya da gama kai. Na kuma tabbata kuna nan dai kuna tunani akan wannan
roko da na yi muku. Ni kam ina nan ina tunani a kansa. Gwamnati tana nan tana
ta tunani a kan yadda za’a yi a karfafa aikin gayya saboda jama’a su taimaki
kansu da kansu. Wadansu daga cikin hanyoyin sune za’a shirya kyautoci iri- iri
wadanda za’a rika bayarwa kowace shekara ga dukkan mutanen da suka fi kowa
himmatuwa wajen gama gwuiwa su taimaki kansu da kansu. Don nuna shekara biyar
da cikar samun mulkin kan wannan jihar, ina so in ba wa kowane daya daga cikin
ku ko a ina yake wannan aiki. Ina so kowa da kowa a cikinku a wannan shekara ya
shuka bishiya a gidansa ko a fili ko a gonarsa wanda a nan gaba za ta ba da
itacen girki ko kuma ‘ya’yan itacen da za’a ci. Shekaru masu zuwa idan muka
zauna a karkashin itacen bishiyoyin, za mu iya tunawa da hijira 1964 a kan
hijira wadda mu da kanmu mun taimaka wajen tattalin arzikin kasarmu. Gwamnati
ba za ta iya ba ku duk abin da ku ke bukata ba, ko kuma kuke so ku samu
ba.Tilas ne ku shirya ku yi abubuwa da dama da kanku. Kuna da kasa wadda take
da ‘yanci da zaman lafiya in da kowa daga cikinku zai ci riba idan ya yi amfani
da gapopinsa da basirarsa. Cigaba abu ne wanda duk ya shafe mu baki daya , ba
sai gwamnati ko En’e kawai ba. Saboda haka ku kudira niyya cewa wadannan
bishiyoyi da za ku dasa su zama alama ce ta nuna sa niyya a kan cigaban kasar
nan.
Bara gwamnatin tarayya da ta jihohi sun hadu sun
kidaya duk mutanen kasar nan. Wannan aiki ne mai wuya da nauyi, to amma na yi
farin ciki da cewa mutane a ko ina a jihar nan sun fahimci muhimmancin samun
kyakkyawar kidayar mutane. Kuma sun amsa kiran gwamnati sun kuma hada kai da
ita. Wannan ya rage nauyin aikin masu kidaya. Gwamnati na ta kara jin karfi
saboda irin wannan hada kai da kuka nuna, kuma tana fata cewa a nan gaba duk
sanda abubuwa muhimmai suka faru za ku nuna sha’awarku da dagewarku.
Na tuna da na yi muku magana bara a watan Maris,
abubuwa mara sa dadi sun faru a kasar Afirka. Galibin abubuwa sun faru ne
saboda son zuciya da kuma rashin dabarar wadansu mutane. Ina fata wadannan
abubuwa ba za su faru a Nijeriya ta Arewa ba. To amma duk da haka ina so in yi
wa duk shugaba wanda yake mulkin jama’a gargadi. Hanyoyin cigaba sun tunkaro da
karfinsu, da yawa daga cikinsu za su yi hankoro su nemi ci da zuci. Tilas ne ku
san yadda za ku yi ku zauna da su. Mutanen da aka dankawa jama’a a hannunsu,
tilas ne su dauki duk nauyin aikinsu, su kuma gane bukatar canji, idan dai
canjin nan shi zai jawowa jama’a alheri.
Tilas ne ku nuna cewa kun cancanci mukamin da ku ke
da su, da yiwa jama’arku bauta, ko da shugaban kuwa Sarki ne ko Minister ko
Hakimi ko Dagaci ko shugaban babbar makaranta ko malamin makarantar kauye, ko
dan sanda ko ma’aikacin baitul mali ne. Tilas ne ku yi aikinku da gaskiya, da
jure wahala cikin tsoron Allah da son kasarku. Da shugabanni da jama’arsu suna
zaman cudeni-in-cudeka ne akan jawowa kasa cigaba. Tilas ne ka da mu yarda saboda
sakewa mu kyale rashin kwanciyar hankali ya bata mana kasarmu. Tilas ne mu
canzja tare da lokaci, kowane lokaci mu rika gyara halin zaman mu in da zai da
ce da zamani, ba tare da mun yi wadansu ra’ayuyyuka ba wadanda ba su dace da
halayar zaman kasarmu ba.
Ni bana shakka a zuciyata cewa cigaban kasarmu zai
karu a kan hanya madaidaiciya, ko da yake a ko wane lokaci, tilas ne a sami
mutane masu son kai da kuma dogon buri wadanda za su so su rudar da jama’a.
Hakkin kowa daga cikinmu ne mu bi ta kan hanyar doka mu nuna musu kuskurensu.
Mu yi kokari kowane lokaci mu rike halinmu na nagarta da fara’a mu kuma yi
kokari mu gyara kowane rudani ne ya faru tsakaninmu, ta hanyar da abokai ya
kamata su yi. Don saboda ko wane bambamci ne yake tsakaninmu, dukanmu mutanen
gida daya ne, yayye da kanne, da abokai. Ina so daga wannan rana kowa daga
cikinmu ya kuduri niyya, ya yi mutukar kokarinsa ya ga cewa kasar nan tamu tana
ci gaba ta hanya madaidaiciya wadda ta haka ne kawai za mu sami biyan
bukatunmu. Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya sa mana albarka baki daya. Amin.”
Idan har kun zo nan a karatunku
ba tare da yin tsallake ko batan layi ba, tabbas na san kuma kun ji wani abu a
zuciyarku, ko da kuwa bai yi daidai da abin da na ji ba. Wannan babban kalubale ne a gare mu, mu ne jikokin su Sardauna, idan har aka ci gaba da tafiya a haka, zuwa lokacin jikokinmu kuma ya abin zai kasance? Allah ya kawo mana
dauki a Arewa da Nijeriya baki daya.