Thursday, January 9, 2014

TALLA: Jama’a Ga Sabon Littafi


Bangon littafin Batulu

Marubucin shafin GADAR ZARE, a jaridar RARIYA  Dakta Auwalu Anwar, ya wallafa littafi mai suna Batulu, littafin na dauke da shafuka dari biyu da sittin da hudu (264), turkashi!

Cikin littafin, marubucin ya yi amfani da yanayin kulluwar dangantaka tsakanin malamai da dalibansu da kuma tsakanin su kan su daliban, a junan su, a jami’o’in Nijeriya a zamanin mulkin farar hula, a jamhuriyya ta biyu, wajen tsara labarin da aka bayar a cikin wannan littafi. Tasirin gwagwarmayar akidu da ra’ayoyi a tafiyar da kungiyoyin siyasar da ake da su a kasa, ga sarrafa tunanin al’uma, ya taimaka ainun wajen fassara irin fahimtar da dalibai suka yi wa matsayinsu a Jami’ar Goron Dutse, wanda a dalilin hakan ta kai suka dinga takun saka da hukumar makaranta, har a karshe aka yi mummunan boren dalibai a Jami’ar. Hukumar makarantar ta yi amfani da wannan tashin hankali don ta sallami wasu daga shugabannin kungiyar daliban da burin tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro.

Hayaniyar takaddama tsakanin dalibai da hukumar jami’ar ba ta hana samari da ’yammata sheke ayarsu tare da mike kafa don kafa tirken shagalin rayuwa a makarantar ba. Ta wannan fuska, an ci lagwadar soyayya an sha wahalarta, an riki alkawarinta an ci amanarta, sau barkatai.

A cikin irin wannan hali na rashin tabbas, aka samu wata daliba mai suna Batulu wadda ta gwanance wajen iya yakin sunkuru da yi wa maneman ta kiwon ragon layya.

Shin Batulu ta kasance sakaina mai iya ruwa don ta dau fansa ne, ko don ta karantar da duniya zurfin makircin mata? Akwai amsoshin wannan tambaya masu bambancin hujjoji a cikin wannan littafi wanda aka rada wa sunan yarinyar, don isuwar muhimmancinta da kasancewa jigon da aka gini labarin a kansa.

An soma shirye-shiryen tsara fim din wannan littafi. Maza ku mallaki naku da wuri, a kan naira dubu biyu da dari biyar (N2,500) mai bangon takarda, ko naira dubu hudu (N4,000) mai bangon kwali. 

Ana iya yin oda daga Kamfanin, ABU Press Limited Zaria, ko Kamfanin Rariya Media Services Ltd, masu buga jaridar RARIYA, a Lamba 53, Titin Mombolo, Wuse Zone 2, Abuja. 

Ana iya kira ko a yi tes ga wadannan lambobi don neman karin bayani: 08032493020, 0803 703 9914, 08065949711 ko a aika da imel ga: adnanwar@libe.com; abupress2005@yahoo.co.uk; abupress2013@gmail.com

Wednesday, January 8, 2014

HOTO: Bashir Ahmad Tare Da Malamansa

King's Hotel, Gusau
Daga Dama, Bashir Yahuza Malumfashi (Aminiya), Muhammad Kabir Assada (Muryar Arewa), Malam Yusuf Dingyadi (Magayakin Garkuwan Sokoto), Badamasi Shu'aibu Buruji (Concern Magazine), Al-Amin Chiroma (Leadership Hausa) da Bashir Ahmad (Rariya), ke taya Malam Dingyadi, murnar karrama shi da aka yi, lokacin taron shekara na 'Dandalin Siyasa Online' karo na biyar da aka gudanar a Gusau, Zamfara. (2013).

Hoto: BY Malumfashi

Tuesday, January 7, 2014

Asari Dokubo: Mahaukaci Da Gata!


Asari Dokubo

Ashafa Murnai Barkiya (Editan Jaridar RARIYA)

A lokacin da na kama hanya zan tafi yi wa mahaukacin Neja Delta, Dokibo Asari intabiyu, da dare ne, bayan na yi sallar Isha’i. Duk wani tarihi nasa na irin na irin kashe-kashen jami’an tsaro da suka hada da sojoji da ‘yan sanda, tabargaza da barnata dukiyar basa da ya yi babu wanda ban sani ba. Asari ya mallaki manyan makaman da yawanci ma wasu jami’an tsaronmu ba su san yadda ake sarrafa su ba. A tattaunawar da na yi da shi, cewa ya yi shi bai ajiye makamai ba, ya dai zauna hutun karon da ya gwabza da maza ne kawai tunda dan’uwansu Jonathan aka ba mulkin kasar nan, dama abin da suke so kenan.

Ni dai na san ban ci maganin bindiga ko na gurneti ba, ballantana layar zana. Haka na yi kumumuwa na afka gidan babban gogarman dan ta’addar kasar nan muka yi doguwar tattaunawa da shi. Jiki na ya fara bari a yayin da yake ratattakar ‘yan Arewa. Ji na yi kawai ina tsima, ina kuma tunanin ta ina zai kai min naushi saboda ni dan Arewa ne? Domin irin yadda yake magana, yana kugi, yana karaji yana zagin ‘yan Arewa, ban yi zaton zan fito gidansa da raina ba, kada giwa ta taka kwado, wato kada ya ce bari ma ya fara da wannan dan tsigigin.

A yadda na fahimci Asari, to duk mai shiryawa ma ya shirya, makamansa na nan jibge, kuma mabiyansa na nan ba su tarwatse ba, tunda dama ya ce min shi bai yarda da afuwa ba, wato shirin amnesty da aka yi wata ‘yan ta’addar Neja Delta. Ranar komawa bakin daga ko ranar komawa aika-aika kawai yake jira. Mai tababar zance na ya farka daga barci, ya je ya sake karanta hirar da na yi da shi, zai tabbatar da haka.

Kada kuma a manta, Asari ya tsine wa Nijeriya, ya ce Allah ya kawo bala’in da zai tarwatsa ta. Amma irin wadannan ‘yan ta’addar ne ke mara wa shugaban kasa na yanzu baya, har yana yi mana barazanar yaki. Sai dai me, ba na ganin laifin Asari, laifin Jonathan nake gani da kuma wadanda suka kinkimo shi. Idan shugaba dai shugaba ne, kai ko da shugaban gidan giya ne, ba zai bari a cikin mashayarsa ya ji gogarman dan takife ko wani dan banzan day a sha ya yi mankas ya rika yin irin kalaman da Asari yake yi ba don goyon bayan shugabancinsa.

Ya ce idan Jonathan bai ci zade ba za a yi yaki a kasar nan? To ni dai ban san yadda Jonathan ke nufi da makomar kasar nan ba, da har yake barin ‘yan’uwansa na yaba bakak-en maganganu dangane da makomar kasar nan. Ko bai san ana yi ba ne? Saboda ganganci har wasu gurzagullan karti ke tsayawa a kan titunanmu da sunan tsaro, ga bindigogi an damka wa kowa. Su kwana bakwai suna bincikar motoci ba su samu ko basilla a cikin kayan wani ba. An yi asarar kudin tsaro kawai! Amma abin haushi ga su Asari can suna kada gangar gangamin tarwatsa kasar nan an kyale su sai iskanci suke yi a Abuja.

Cikin shekarun nan biyu duk wani dan Arewa ya san cewa Abuja ta koma Abu-baka! Saboda wasu bakaken halittu masu bakaken kaya sanye da b akaken huluna sun cika garin, ko kuma sun yi wa ko’ina a cikin birnin kaka-gida. A Abuja duk ma’aikatar da ka shiga da rawani, to ka tabbata a ranar ka raba hanya da sa’a. Amma idan kana so a dauke ka da mutunci, to ka sa bakar hula ka shiga wata ma’aikata ko da kuwa dan Arewa ne ke shugabantar ta.

Muna da ministan tsaro, Sufeto Janar na ‘yan sanda da kuma shugaban SSS. Ga mahaukaci da sanda ya kutsa cikin kasuwa amma sun sa masa ido sai dukan mutane yake yi. Amma da wani dan jarida ne ya yi biji-biji da Jonathan, to shikenan ya yi laifi. Da gwamnoninmu mu suke wakilta, ya kamata a ce sun yi taron gaggawa sun tsine wa Asari Dokibo, tunda yana neman kasar nan da bakar fitina. Sannan su gaggauta umartar shugaban kasa ya nisanta kansa da shi. Su ma wakilanmu na majalisar dattawa da na tarayya duk su yi haka. Sannan su tilasta wa Sufeto Janar na ‘yan sanda ya gaggauta kama Asari Dokubo. Ammma ya muka iya da ranmu? Na ji majalisa ta bada umarni.

Tun da gwangwanaye gare mu ba gwamnoni ba. Kuma ’yan zaman majalisa gare mu ba ‘yan majalisa ba? Idan ba a kama shi ba babu abin da za su yi. Shi kansa Sufeto Janar din idan har sufeton da ya sufetantu da sufetacciyar akidar aikin dan sanda ne, ya kamata a ce ya kama Asari Dokubo.

To ai dama Bahaushe ya ce idan ka ga mahaukaci da makami, yana yadda ya ga dama, to yana da gata shi ya sa ba ya tabuwa, kuma ba ya kamuwa. Maganar nan fa gaskiya ce, tunda kuwa an ce rikon mahaukaci sai sarki. Shin Asari Dokubo mahaukacin wane ne?

An buga wannan rubutu a shafin Gyaran Ganga a jaridar RARIYA, kuma rubutun hakkin mallakar jaridar ne.

Ko Wa Ya Kaiwa Mahaifin Gwamnan Kano Hari?


Gwamna Rabiu Kwankwaso
Wani labari da jaridar RARIYA ta labarto ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba, sun kai wa mahaifin mai girma gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Alhaji Musa Kwankwaso, farmaki, a daren jiya, sai dai Allah bai ba wa wannan ‘yan ta’adda ikon kashe mahaifin gwamnan ba, sai dai sun harbi mutane da dama a hanyarsu da kai masa harin.

Alhaji Musa Kwankwaso, shi ne hakimin karamar hukumar Madobi, kuma yana rike da sarauta mai daraja ta ‘Maji Dadin Kano’ a fadar mai martaba Sarkin Kano.

Shin ko wane gungun ‘yan ta’addane suka kai wa Maji Dadin Kanon wannan farmaki?

Allah ya kara kare mu, ya kara kawo mana zaman lafiya a jiharmu Kano da kasarmu Nigeria baki daya.

The Top Five Countries to Visit in 2014



If you’re in the mood to do some international traveling, there are many exciting countries worth visiting. The world is always changing, and some destinations are especially appealing right now. According to Lonely Planet, the following are the ten best countries to visit in 2014.
Brazil
1. BRAZIL - There are many good reasons to visit Brazil in 2014, starting with the FIFA World Cup. Even if you’re not a sports fan, however, this growing country has a great deal to offer. It features some of the world’s most beautiful beaches such as Copacabana and Ipanema, as well as an always exuberant nightlife. If you go early in the year you can also experience the world’s biggest Carnival celebration in Rio de Janeiro

Scotland
2. SCOTLAND - Scotland is always a memorable place to visit, but in 2014 it is especially exciting. Over the summer, you can catch the Commonwealth Games in Glasgow if you are in town. There are also a myriad of other events and festivals, including the Spirit of Speyside Whiskey Festival in the spring and the government sponsored Year of Homecoming festival. The nation has also recently upgraded its transportation system and opened some new sports venues to make it even more visitor friendly.
Malaysia
3. MALAYSIA - Malaysia has one of the fastest growing economies in Southeast Asia. Aside from its many historic and natural attractions, the nation has recently opened some notable new sites. These include Legoland Malaysia and Melaka, a bird park that contains hundreds of species of birds. This is a great year to visit Malaysia, especially as you can now find reasonable fares by airlines such as AirAsia and Malaysia Airlines. 
Sweden
4. SWEDEN - Sweden is one of the most fascinating destinations in Northern Europe right now. In addition to the distinctive Scandanavian landscape, you will find all kinds of cultural attractions in cities such as Stockholm and Umea, which was named the European Capital of Culture for 2014. Sweden’s cities are full of lively clubs, museums and cafes. You can also enjoy the nation’s distinctively fresh cuisine, which includes local cheeses, produce, game and seafood.
Antarctica

5. ANTARCTICA - The world’s coldest and least populated continent has a lot to offer adventurous travelers. While not necessarily a country – it is a destination travelers should consider for 2014. Antarctica is one of the few regions where you can appreciate the stark beauty of nature with hardly any distractions. There is the fascinating wildlife, such as leopard seals, killer whales, seabirds and, of course, penguins. You can also experience the grandeur of glaciers, giant icebergs and mountain ranges that have never been scaled. An Antarctic cruise is a travel experience unlike any other, and is worth putting on your bucket list for 2014.