Sunday, May 4, 2014

My ‘Sambisa’ Tale – Chibok Girl

It was going to be like a normal night

It was going to be a chat with my fellow girls until I give-in to sleep

It was going to be a night with Amina, Fatima and Hauwa

Just a normal night… just after I said my little prayer 

A night when the moon couldn’t whisper to my innocent heart like every other night

A night when my dreams will be engulfed by the darkest night

Have my innocent heart committed a crime to chase that dream?

If achieving my goals through education is forbidden, would an early marriage be acceptable?

If regrets could turn back the hands of time

If wishes could make the watchman not feel drowsy on duty

Oh! I wished my life never depended on the weak index of that soldier (God bless his efforts)

Or on the frail fence where we even jump over sometimes.

In my sleep I heard strange voices; on my feet was a tap…

‘HE’ touched me… Mama! He touched me!!!

Screams went louder from different sections; I closed my eyes and wished it was a dream

Lo and Behold! The very aspiration and my pursuit for empowerment delivered me unto ‘HIM’.

I reached out to Hauwa to at least be on same four-wheeled truck to share from her courage

Instead my worst fears gripped me as I heard more Horror and masculine voice

Gunshot loudly mellowed our screams for help

Could I have jumped off like Fatima and Amina; I thought of it but I couldn’t dare…

How can this same language they speak become foreign to me?

I called on same Allah as they too scream…

Does a different blood flow through their veins?

My heart beat stopped several times yet my thoughts were wide.

The sounds of Crickets and strong wind; cries and prayers proved we were going deep

Deep into Isolation; deep into a cave we talked dreadfully of in our little girl’s gossip

The plague I once feared has come upon me

What is forbidden? Is it my aspirations, HIS Hellish ideology or what I have been subjected into right now?

Father! I need now more than ever your love to rescue me from this hate

It’s the 7th day so far and for the first time in my tender life I have seen my period in the forest

Mama! Oh! Mama… they wouldn’t let me do what you have taught me.

Mama you have no idea what HE has done me…

I heard some of us have died… some of starvation and some from deep wounds

Mama, it’s going to be my turn tomorrow…

I contemplate suicide, would HE do this to me?

Mama it’s cold out here, I feel pains on my chest am I going to die?

You will not be wrong if you think we have taken oaths…

The heights of all imaginations have been done to me Mama…

I will be 13years tomorrow and I have seen it all

Mama, my tender eyes have seen the other side of Life

Be strong Mama, I have tried not to give-up…

Be brave as you have taught me to be

If I see you again, please don’t ask me what has happened to me.

If not mama, know that the worse is yet to happen because I choose not to give-up.

The stars will never shine bright again…

The moon will set at noon…

The cock will crow at Midnight…

It will never be the same again….

But I love you Mama!!!

...Dedicated to the abducted Chibok girls. #BringBackOurGirls

Monday, April 28, 2014

HIRA TSAKANIN BABAN DA MAMAN FAISAL KAN JARUMAN FINAFINAN HAUSA


Hira tsakanin miji (Baban Faisal) da maidakinsa (Maman Faisal) akan jaruman finafinan Hausa da suke goyon baya.

"Kai Safiya gaskiya fa duk 'yan fim din Hausa babu mai birge ni kamar Zainab Indome"

"Lallai maigida na ga kana yawan sayo fina finan da ta ke ciki"

"A she dai kin lura?"

"Haba Baban Faisal ai na dade da lura da haka"

"Wato Dear ko bata min rai kika yi idan na kalli idanuwan Indome sai na ji na huce"

"Ok shi ya sa na ga daga mun sami matsala ko ba wuta sai ka tayar da inji ka sanya fim din ta.?"

"Kwarai ma kuwa, ba ma kamar a ce fim din da ta ke dan rausayawa, kin san ta iya rawa"

"Gaskiya kam Zainab Indomee ta yi"

"Ga ta duk kayan da ta sanya sai ki ga ya yi daram a jikin ta.

"Gaskiya Baban Faisal ka gama yarda da alamarin Zainab Indome"

"A zakin murya kuma idan kika sami Nafisa sai wata rana an gama,"

"Kai maigida Nafisa har wani dadin murya ne da ita?"

"Kwarai ma kuwa idan ta na magana kamar ta na rera waka"

"Hm Baban Faisal ba ka da dama"

"Kin san kuma wa ta fi kira da diri?

" Sai ka fada maigida"

"Na ba ki gari sahibata Safiya"

" Maigida ai ni a duniya babu mai birge ni kamar Ali Nuhu, ban taba ganin namijin da a duniya ya iya sanya kaya kamar Ali nuhu ba. Babu ma kamar idan ya sanya kananan kaya, wani fim da ya sanya wani wando iya gwiwa har tsayar da wajen na yi dan kawai na sha kallo........."

" Ke Safiya ki na da hankali kuwa?"

" Haba Baban Faisal da hankalina mana, rawa kuma da iya girgiza ban taba gajiya da kallon Adam Zango ba, A jikin sa kuma kasumbar da ya ke bari ita ta fi daukar min hankali"

"Safiya dakata ya isa haka, wace irin magana ce wannan ta rashin hankali?"

" Baban Faisal yadda ka dire dole nima sai na dire, ba rashin hankali a ciki. Murmushin Maishunku kuma shi ke sanya ni nutsuwa a duk lokacin da ya yi"

" Idan kika sake magana sai na shake ki 'yar iskar banza kawai"

" Baban Faisal sahibi ko kashe ni za ka yi wallahi sai na kai karshe yadda yadda ka dire na ka. Abinda ya sa kuma ka ji ban rabuwa da wakar Alan Waka ko da a bandaki na ke kuma ko muna tare muryar sa na sumar da ni gaba daya, wani lokacin sai na ji kamar na yi mutuwar tsaye"

" Gaskiya Maman Faisal kin yi gamo da bakaken aljanu, wannan rashin hankali har ina, wadannan maganganu na ki kare ba zai ci ba, sai ka ce arniya"

" Kar ka hada ni da arniya, kafi kowa sanin ni musulma ce kamar kai"

" To lallai ki na bukatar a yi miki rukiyya ko kuma aje wajen malamai su rubuta miki Innahu Ala Rajaihi lakadir kafa bakwai bakwai na kwana bakwai"

" Lafiya ta ras"

" To kuwa ba karamar 'yar rainin wayau ba ce ke kuma dole manyan ki su san wannan maganar gaskiya ba zan lamunce ba wallahi, haba sai ka ce a garin gaba gaba, ki na matar aure ki na fadin wai ki na sha'awar mazan waje dan iskanci, daga yau ma ba za a sake kallon fim a gidan nan ba"

...Shin tsakanin Baban Faisal da Maman Faisal wane ne ya fi gaskiya?    

GAYYATA!!!

INTEGRITY ICONS INTERNATIONAL na farin cikin gayyatar daukakin jama'a zuwa laccar shekara-shekara karo na biyu ta SAM NDA-ISAIAH, mai taken "Adalci Da Kyautatuwar Shugabanci Shi Ke Kai Kasa Ga Gaci".

•Babban mai masaukin baki, Mai Girma Gwamnan jihar Sokoto, Aliyu Wamakko, (Sarkin Yakin Sokoto).

•Karkashin jagorancin shugabancin Kakakin Majalisar Tarayya, Hon. Aminu Waziri Tambuwal, (Matawallen Sokoto).

•Uban Taron, Mai Alfarma, Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na III.

•Uwar Taron, Dr. Baraka Sani, tsohuwar kwamishiniyar noma ta jihar Kano.

•Bako mai jawabi, Dr. Tukur Muhammad Baba, na Jami'ar Usmanu Danfodio.

•Manyan Baki na Musamman, Alhaji Shehu Usman Shagari (Turakin Sokoto), tsohon shugaban kasa, Bishop Mathew Hassan Kukah.

>Rana: 1 ga Mayu, 2014
>Lokaci: 11:00 na rana
>Wuri: Sultan Maccido Institute for Qur'anic & General Studies, Sokoto.

Don Karin Bayani Tuntubi:
-Muhammad Saidu Etsu - 08069789087
-Bashir Ahmad - 08032493020
-Abdulmumin S. Balogun - 08069727798
-Sadauki Abubakar Gawu - 08057009909

Monday, March 24, 2014

National Conference: Youngest delegate at Confab, Yadomah Mandara, pledges to Start a foundation with allowance

As a delegate to the National Conference – the youngest of them all, i am humbled to be part of the process of making my country better, I am willing to make modest sacrifices so that my generation and generation yet unborn can live in better country.

The Federal Government has rationalized that delegates should be paid sitting allowances, in all honesty I am modestly comfortable and able to cater for my immediate needs. Some of my colleagues have indicated their intention not to receive the money which in itself is a pointer to the fact that we still have men and women with high redeeming qualities among us.

However, I am not unmindful of the appalling poverty and great need that exists where I come from and the people I represent. We have a situation where widows and orphans have been abandoned by society, these are individuals made vulnerable by the insurgency. They have no idea how to pay the school fees of their children and wards, and how to eat at least once a day. We have a scenario where things we take for granted mean the world to others – physically challenged people who will never be able to afford wheel chairs and thousands of people who can’t afford medical care because they are poor and have been injured by terrorists. I want them to consider my sitting allowance as a gift to them and humanity.

I do not do this for praise nor to look good in the eyes of the society, I am doing this because it is the right thing to do. I have received my first payment which is the sum of 1,460,000 naira yesterday evening (21st March 2014) from the National Conference.

I hereby pledge to use my allowances as a seed grant and start a foundation that will cater for vulnerable women especially widows and children in Borno State, if you understand their hopeless and helpless state in Borno State and Northern Nigeria in general you will support me in this new drive to put a smile on their faces.

Friday, February 21, 2014

Sharhin Littafin Batulu

Marubuci – Auwalu Anwar
Shekara – 2013
Sunan Littafi – BATULU
Madaba’a – ABU Press Ltd
Shafuka – 264
Mai Sharhi – Halima Musa

BATULU littafi ne da aka wallafa a shekara ta dubu biyu da goma sha uku. Marubucin littafin, Dr. Auwalu Anwar, ba bako ba ne ga duk wani makarancin rubuce-rubucen Hausa. Hasali ma, sanannen marubuci ne wanda ya wallafa kasidu da littattafai da wake-wake da dama. Haka shi malamin tarihi ne wanda ya koyar a jami’ar Maiduguri. Bugu da kari, wasu za su iya tuna shi a matsayin marubucin sharhin GADAR ZARE a jaridar Rariya.

An zayyana labarin BATULU a cikin shafuka dari biyu da sittin da hudu. An kuma kasafta shi babi-babi har ashirin da biyar, ta yadda kowane jigo ya kasance babi daya, da takensa, tare da jero su bibiye da juna yadda labarin ya dinga hauhawa, har karshe. Wannan ya bai wa mai karatu damar hangen abinda kowanne babi zai kunsa.

Littafin ya dace da matasa, ’yan jami’a, samari da ’yammata, har ma da masu burin zuwa jami’a. Saboda su babban jigon labarin ya fi shafa don ya zama ishara. Amma iyaye ma wannan littafi zai musu matukar amfani don su san abubuwan da ke wakana a kusurwoyin jami’o’in da ’ya’yansu ke karatu da kuma abin da ’ya’yansu ke aikatawa da hatsarin da za su iya abkawa ciki. Makarantan littafin baki daya, za su amfana ta hanyar fahimta da kuma kiyaye musabbabin faruwar wasu al’amura a jami’o’i.

Marubucin littafin ya yi amfani da salon zance mai sauki wajen gabatar da shi. Ya yi amfani da Karin Magana sau da dama wajen isar da sakon da ya ke muradin isarwa ta yadda duk wani mai jin Hausa zai iya karantawa ya fahimta. Saukaka salon rubutu da marubucin ya yi, ya kasance tamkar kwarin gwiwa ga mai karatu. Haka ya yi amfani da salon tattaunawa da zancen zuci, wanda ya kara kawata, ya kuma saukaka bin labarin ga mai karatu. Akwai ’yan wuraren da ya yi amfani da kalmomin Larabci (kamar wurin da ake maganar hubbul Nabiyi da hubbul nafsi da hubbul malu). Ko kadan hakan bai takaita saukin fahimtar littafin ba. Wani abin sha’awa ma, sai amfani da Larabcin ya kara kayatar da sakon da marubucin ke kokarin isarwa.

Duk wanda ya karanta BATULU zai yi mamakin yadda marubucin ya fede biri har wutsiya dangane da yanayin rayuwar dalibai a jami’a. Musamman badakalar soyayya tsakanin dalibai, tsakanin dalibai da malamai da kuma tsakanin dalibai da jama’ar gari. Abin mamakin a nan shi ne, yadda ya bayyana yaya fasikanci ke wakana karara tsakanin rukunin wadannan bayin Allah. Musamman tsakanin dalibai mata da malamansu, ta yadda ake shakuwa da cin amana da yaudara. Wannan hakika ya jaddada tunani da kuma muguwar fahimtar da mafiya yawan jama’a ke yi wa daliban jami’a mata. Yawanci ana yi musu kallon ’yan iska kuma watsattsu marasa mutunci da kunya. Hakan na iya kara tunzura masu ikirarin hana ’yayansu mata zuwa jami’a don tsoron kar su lalace, har sai sun yi aure. Wadanda suka dauki abin da zafi ma, wannan na iya sa su hana ’ya’yan nasu mata zuwa jami’ar dungurungun da zimmar kare mutuncinsu.

Hausawa sun ce duniya zaman marina ce. Watau kowa da inda ya sanya gabansa. Duk cikin hayaniya da badakalar soyayya, har ma da fasikancin da ake yi a jami’ar Goron Dutse, marubucin ya iya nuna cewa ba duka aka taru aka zama daya ba. Misali, marubucin ya gabatar da hazikan dalibai da ke dawowa da dakon littattafai daga wajen karatu da tsakar dare, daidai lokacin da ake dawo da wasu ’yan’uwansu dalibai daga dabdala da sharholiya cikin motoci na alfarma. Ya kuma iya zakulo da bayyana mutuntaka da da’a da tarbiyya ta gari, ta hanyar wasu taurari da suka kasance dalibai mata, masu kamun kai da nuna kyama ga halayen ashsha da takwarorinsu, suka dulmiya a ciki. Watakila kasancewar wasu daga cikin wadannan dalibai jinsin Fulbe, ya bankado dan abin da ba a rasa ba, na kyashi da kushe tsakanin kabilun Hausawa da na Fulani, sabanin gamayyar dole da ake yi wa kabilun biyu.

Idan manufar marubucin ya bayyana ruguntsumi da dambarwa da kwamacala da yaudara da munafunci da cin amana a soyayya ne, to lallai ya cim ma burinsa. Haka ya cim ma nasarar bayyana irin gumurzun da ke wakana tsakanin hukumomin jami’o’i da kungiyoyin dalibai, da kuma tsakanin malaman da hukumomin kasa. Kamar yadda abubuwa suka kasance a jami’ar Goron Dutse, tabbas haka suke a jami’o’i da dama a zahiri.

BATULU littafi ne da za a iya gabatarwa ga kowanne irin makaranci saboda akwai darussa masu yawa a cikinsa. Babban darasin shi ne, mutum ya yi takatsantsan a harkokin soyayya. Saboda mayaudara sun yawaita a duniya ba ma a jami’a kawai ba.

An yi amfani da taurari da dama wajen isar da sako a BATULU. Manyan taurarin dai su ne Amadu da Batulu. Duk dambarwar cikin littafin ta rayuwarsu ce. Sai kuma sauran kananan taurari da aka yi amfani da su wajen karin bayanai, wadanda suka kasance kawaye, ko abokanai ko kuma malamai ga masoyan, har ma da iyayen manyan taurarin.

Idan ana maganar jigo, akwai su da dama. Babban jigon dai su ne Yaudara da Munafunci. Marubucin da kansa a karshe ya tari numfashin mai karatu da ya canza wa Batulu suna zuwa “Butulu”.
Wanda kusan duk mai karatu zai yanke wannan hukunci tun kafin ma ya kai karshen littafin. Akwai kuma irin wannan yaudara da ta wakana tsakanin Batulu da Malam Bello. Wasu na iya ganin soyayya a matsayin babban jigon BATULU. Wannan za ta iya kasancewa. Saboda an dabaibaye labarin cikin harkokin soyayyar da ta kasance tun farko tsakanin Batulu da Salisu, ta kai kan Malam Bello, sai kuma Amadu, Sai Musa, ta kuma kare a kan Iliyasu. Akwai jigon siyasa da rarrabuwar akidar mutanen birnin Kano tsakanin masu bin akidar siyasar gurguzu da kuma ta jari hujja. Haka kuma ta kasance a siyasar jami’ar Goron Dutse, tsakanin malamai da kungiyoyin dalibai. BATULU kuma ya kunshi jigon rarrabuwar jama’ar garin Kano tsakanin ’yan boko da malaman addini da ’yan kasuwa (wadanda aka fi sani da ‘alhazan birni’), inda ya kyankyashi jayayya da gasa da ke tsakanin wadannan rabe-raben, ko gungu-gungun al’umma, wajen neman abin duniya.

Duk wadannan jigogin marubucin ya tubka su cikin labarin da ya bayar ta hanyar alakanta su da taurari daban-daban, kamar abokanai da kawaye da malamai da ma iyayen manyan taurarin littafin. Haka jigogin da suka shafi al’adu sanannu ne ba sababbi ba ga yanayin rayuwar garin Kano da ma na sauran al’umma baki daya.

Marubucin ya gabatar da zubi da tsarin BATULU daidai yadda ya dace da yanayin halayyar taurarin littafin da kuma yadda karshen labarin ya kasance. Ta yadda mai karatu zai kagara ya ga yadda za ta kaya, tare da jefo ba-zata a wasu lokutan. Ya kuma yi amfani da nau’o’in hatsari wajen kawar da wasu taurarin wadanda ci gaba da kasancewarsu, za ta haramta warware sarkakiyar cikin littafin. Misali, boren daliban jami’ar Goron Dutse ne ya kawar da Tanko daga labarin, kamar yadda faduwar Salisu jarrabawa ta kawar da shi daga labarin. Haka shiryeyyen tashin hankalin ashararai da ’yan iskar garin Kano ya kawar da Malam Bello daga labarin.

Shi dai Littafin BATULU an gabatar da shi ne a jami’ar Goron Dutse da ke garin Kano. Kusan duk manyan abubuwan da suka wakana a nan suka wakana, sai wanda ba a rasa ba. Wannan kamar wani sabon abu ne. Domin yawancin marubuta suna amfani da sunayen kirkira ne, ba sunayen gaske na garuruwan da aka sani ba. Hakan ta sa mai karatu ganin kamar yana cikin labarin, musamman idan a Kano ya ke zaune, ko ya san garin.

Saura da me? Sai masu karatu su nemi BATULU, don ganewa idanuwansu, kacokan, wainar da ake toyawa a jami’ar Goron Dutse ta Kanon Dabo birni.


Ana iya yin oda daga Kamfanin ABU Press Limited Zaria, ko Kamfanin Rariya Media Services Ltd, Lamba 53, Titin Mombolo, Wuse Zone 2, Abuja.

Don karin bayani za a iya kira ko a yi tes ga wadannan lambobi: 08032493020, 08037039914, 08065949711 ko a aika da imel ga: adnanwar@live.com; abupress2005@yahoo.co.uk; abupress2013@gmail.com