
Gwamnan babban bankin kasa CBN Malam Sanusi Lamido Sanusi wanda a ranar Juma'a da ta gabata Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Dr. Ado Bayero ya nada shi a matsayin Dan Majen Kano ya koma bakin aiki birnin tarayya Abuja cikin kayan sarauta, wato sanye da babbar riga da alkyabba gami da rawani mai kunnuwa biyu sanye a kansa, ga kuma sandar ban girma rike a hannunsa na dama.
Da shigarsa wurin aikin nasa sauran abokan aikinsa da suke karkashinsa sun zo sun karbi gaisuwa irin yadda ake yiwa sarakuna a yankin kasar Hausa.
Muna kara yiwa Malam Sanusi Lamido Sanusi addu'ar Allah ya taya shi rikon wannan sarauta, Allah kuma ya sa wannan sarauta mataki ce a gare shi.
No comments:
Post a Comment