
Gwamna Alh. Aliyu Magatakarda Wamako ya sake komawa kujerarsa ta gwamnan jihar Sokoto a karo na biyu. Wamako na daya daga cikin gwamnoni biyar da kotu ta sauke daga mukaminsu a baya bayan nan.
Jami'un adawa sun bayyana rashin amincewa da zaben tun kafin a bayyana sakamakon zabe a jiya, jami'un na adawa sun bayyana cewa an sace musu wakilansu, wasu kuma an tirsasa su wurin sa hannu a takardar sakamakon zaben.
Gwamna Wamako, ya ce duk wanda bai yarda da sakamakon zaben ba to ya garzaya kotu.
Kai lallai PDP power!!!
No comments:
Post a Comment