Sunday, June 8, 2014

ABIN LURA: Allah Ne Ya Zabi Sanusi Lamido Ba Kwankwaso Ba

Bari na fara wannan rubutu na wa da wasu baitocin waka, da suka yi daidai da abinda zan rubuta....

"Fatan Mai Rabo Guda Ne Baya Fada,
Don Kowa Ya ja Da shi Sai Ya Bar Masa,
Koda Dambe Ne Bare Filin Kokawa,
Kowa Zai Karo Da shi Sai Ya je Kasa,
Gode Wa Ubangiji Don Shi Yai Maka,
Domin Ka Sani Ma Nema Wasu Sun Rasa."

A karshe dai, bayan shekaru 51, Kano ta sake yin sabon Sarki, hakan kuwa ya faru ne bayan rasuwar marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero a ranar Juma'ar da ta gabata, wanda Allah ya bawa sabon Sarkin shi ne Mai Martaba Sanusi Lamido Sanusi, tsohon gwamnan babban bakin CBN. Sai dai wasu na ganin Sanusin ba shi ne ya cancanta ba, hasalima gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso ne ya yi amfani da damarsa, ya yi karfa - karfa ya kakabawa Kanawa, Sanusi a matsayin sabon Sarki. Hmm, ni dai kam ina da ja akan hakan.

 Maganar gaskiya, mafiya yawan jama'ar Kano, ba sa goyon bayan nadin Sanusi Lamido Sanusi a matsayin sabon Sarkin da zai jagorance su, kuma suna da dalilin su na yin hakan. Ko ni har ga Allah a zuciyata na fi so daya daga cikin 'ya'yan marigayi Sarkin Kano ya gaje shi saboda wani dalili na wa. Amma hakan bai sa na gamsu tare da yin addu'ar fatan alheri ga Sanusi Lamido a matsayin sabon Sarkinmu ba. Ba don komai ba sai don saboda na san Allah shi ke bada mulki ga wanda ya so, kuma a lokacin da ya so. 

Duk karfin Sanusi, kudi da mukaminsa bai isa ya sa ya bawa kansa mulki ba, misali Sanusi ya rike mukamin gwamnan babban banki har na tsawon shekaru 5, amma hakan bai sa ya zama Sarkin Kano ba, sai lokaci da shugaban kasa, ya dakatar da shi, ko kuma na ce wa'adinsa ya kare, sannan Allah ya nufa zai zama Sarkin, kuma ya zama.

Kuma mu tuna cewa, da Gwamna Kwankwaso zai iya yin karfa - karfa ya dora wani ya zama Sarki, to ko tantama ba zan yi ba, da mahaifinsa, Mai Girma, Alhaji Musa Saleh Kwankwaso ne zai zama sabon Sarki, tun da kuwa, shi ma basarake ne. Na san za ku amince da haka, saboda kuwa duk irin soyayyar da Kwankwaso yake yi wa Sanusi, ba ta kai wanda yake yi wa mahaifinsa ba.

'Yan uwana Kanawa na san abin akwai ciwo a zuciya, ga shi Allah ya dauki ran Sarkinmu da kowa yake so, sannan wanda ba ma so saboda wani dalilai ya zama sabon Sarkin.

...Sai dai na lura da cewa da yawa daga cikin mutanen da ba a Kano suke ba, suna matukar goyon bayan Sanusin a matsayin sabon Sarki, kuma su ma na hakikance suna da kwararan dalilan su.

Allah ya zaunar da Kano lafiya!!!

Wednesday, June 4, 2014

SABON SALO: Sam Nda-Isaiah Zai Tattauna Da 'Yan Nigeria Kai Tsaye A Facebook

 Sam Nda-Isaiah, dan takarar shugabancin kasa a APC, zai tattauna da ku kai tsaye a shafin sada zumunta na Facebook.

Wannan dama ce ga 'yan Nigeria, ta wannan shirin za ku iya yi wa Sam duk wata tambaya da kuke bukatar amsarta daga gare shi, kuma ku samu amsa nan take.

Tattaunawar za ta kasance a gobe Alhamis 5th Yuni, 2014  da misalin 10:00am - 12:00pm da kuma 2:00pm - 3:00pm.

Lokaci ya yi da za ku ke shigowa ana damawa da ku a harkokin siyasar Nigeria, domin bada gudunmawa wajen samun canji na alheri.

Monday, June 2, 2014

Sam Nda-Isaiah Zai Tattauna Da Jama'a Kai Tsaye A Shafukan Sada Zumunta

 
#TAMBAYISAM (Tattaunawa)

Sam Nda-Isaiah dan takarar shugaban kasa a APC zai tattauna da ku kai tsaye game da takararsa da kuma Nigeria
____________________________________
* Facebook: Alhamis 5th Yuni, 2014 | 10am - 12pm da 2pm - 3pm
____________________________________
* Twitter: Asabar 7th Yuni, 2014 | 4pm - 7pm
____________________________________
* Google+: Laraba 11th Yuni, 2014 | 10am - 12pm

>>> AIKA TAMBAYA TA WADANNAN HANYOYI

Twitter: @SamNdaIsaiah ko @Sam4Hausa

Za kuma a iya amfani da wannan alama #ASKSAM a wadannan shafuka a yayin da tattaunawar ke gudana.

Friday, May 9, 2014

Janar Muhammadu Buhari Kan Sace Daliban Chibok

A dai-dai wannan lokaci da shuwagabannin duniya suke kawowa Najeriya dauki, wajen gani an nemo daliban Cibok mata wadanda aka sace su kusan 300 a makarantarsu ta Sakandare, dan siyasa, tsohon shugaban kasa kuma daya daga cikin shuwagabannin jam'iyyar APC Janar Muhammadu Buhari mai ritaya ya fitar da sanarwa.


"A makonnin da suka wuce, sace dalibai mata da akayi a Cibok, Jihar Borno ya nuna a fili irin barazanar da muka dade muna fama da ita a kasar nan, daga ayyukan mutanen da basu fahimci Musulunci ba.

Addu’o’in mu suna tare da iyalen wadanda suka rasa ‘yan uwansu a wannan tashe-tashen hankula da muke ta gani. Sannan kuma muna mika alhininmu ga iyayen da ‘ya’yansu suke cikin hannun wadannan mugayen mutane.

Wannan mummunan bidiyo da aka saka a yanar gizo, ya nuna a fili cewa shaidanun mutanennan basu da zuciya. Ya nuna ko suwaye su a fili, kuma maza kamar wadanda bai kamata a ce suna keta diyaucin kasa ba. Daga abubuwan da suka nuna, ya fito fili cewa babu Allah a zuciyarsu. Basu da nufin kirki ga kasarmu. Ni Musulmi ne, kuma ina aiki da koyarwar addinin Kirista ma, ta yin amfani da koyarwar addinan guda biyo domin zaman lafiya da kowa da kowa a duniya.

Ina mai sha’awar jaddada matsayi na, na sukar wannan ta’asa wanda bashi da waje duniyar bil-adama. Addinin Musulunci bai amince da shi ba, kuma babu wannan a cikin Bible.

Ya kamata mutanen nan su sani cewa duniyar wayayyu na adawa da ta’addanci. Muna matukar godiya da duniya take goyawa Najeriya a wannan matsanancin lokaci. Muna fata da addu’a na cewa wadannan yara mata zasu koma wajen iyayensu a kwanaki masu zuwa.

Yayin da gwamnatin Tarayya da sojoji suke aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan kasa a wannan lokaci, munyi imanin cewa za’a iya kara matsa lamba wajen gani an tabbatar da tsaron Najeriya da ‘yan Najeriya. Saboda haka muna farin ciki da gwamnatin Tarayya ta amshi taimakon kasa da kasa wajen nemo wadannan dalibai, da kuma kawo karshen ta’addanci a wasu bangarorin Najeriya.

Nayi yaki domin hadin kan Najeriya. A shekaru na masu yawa, ina son tattaba kunne na, da naku tattaba kunnen, da matasa da ma duka ‘yan Najeriya su albarkata daga kasa mai cigaba da hadin kai, da kuma kyamar tarzomar bangaranci a cikin gida, da ma daga kasashen ketare.

Yanzu ba lokacin siyasa bane. Yanzu kuma ba lokacin nuna yatsa bane saboda ban-bancin akida. Hadin kan Najeriya ba abune na wasa ba, kuma babu abunda zai raba mu a matsayinmu na mutanen kasa daya. Saboda haka ina kira ga ‘yan Najeriya a gida, da ma kasashen ketare su goyi bayan kasa a yunkurin da takeyi na kawo karshen hare-hare akan fararen hular da basu ji ba, basu gani ba.

Sai mun ajje a gefe, duk wani buri namu, mun tabbata kasarmu ta hada kanta, ta kwato diyaucinta. Banda ma haka, sanin dukkaninmu ne cewa bamu da wata kasa banda Najeriya da zamu iya kira namu.

Allah Ya albarkaci Najeriya."

#KuDawoManaDaYaranmu #BringBackOurGirls

Daga VOA Hausa

Sunday, May 4, 2014

My ‘Sambisa’ Tale – Chibok Girl

It was going to be like a normal night

It was going to be a chat with my fellow girls until I give-in to sleep

It was going to be a night with Amina, Fatima and Hauwa

Just a normal night… just after I said my little prayer 

A night when the moon couldn’t whisper to my innocent heart like every other night

A night when my dreams will be engulfed by the darkest night

Have my innocent heart committed a crime to chase that dream?

If achieving my goals through education is forbidden, would an early marriage be acceptable?

If regrets could turn back the hands of time

If wishes could make the watchman not feel drowsy on duty

Oh! I wished my life never depended on the weak index of that soldier (God bless his efforts)

Or on the frail fence where we even jump over sometimes.

In my sleep I heard strange voices; on my feet was a tap…

‘HE’ touched me… Mama! He touched me!!!

Screams went louder from different sections; I closed my eyes and wished it was a dream

Lo and Behold! The very aspiration and my pursuit for empowerment delivered me unto ‘HIM’.

I reached out to Hauwa to at least be on same four-wheeled truck to share from her courage

Instead my worst fears gripped me as I heard more Horror and masculine voice

Gunshot loudly mellowed our screams for help

Could I have jumped off like Fatima and Amina; I thought of it but I couldn’t dare…

How can this same language they speak become foreign to me?

I called on same Allah as they too scream…

Does a different blood flow through their veins?

My heart beat stopped several times yet my thoughts were wide.

The sounds of Crickets and strong wind; cries and prayers proved we were going deep

Deep into Isolation; deep into a cave we talked dreadfully of in our little girl’s gossip

The plague I once feared has come upon me

What is forbidden? Is it my aspirations, HIS Hellish ideology or what I have been subjected into right now?

Father! I need now more than ever your love to rescue me from this hate

It’s the 7th day so far and for the first time in my tender life I have seen my period in the forest

Mama! Oh! Mama… they wouldn’t let me do what you have taught me.

Mama you have no idea what HE has done me…

I heard some of us have died… some of starvation and some from deep wounds

Mama, it’s going to be my turn tomorrow…

I contemplate suicide, would HE do this to me?

Mama it’s cold out here, I feel pains on my chest am I going to die?

You will not be wrong if you think we have taken oaths…

The heights of all imaginations have been done to me Mama…

I will be 13years tomorrow and I have seen it all

Mama, my tender eyes have seen the other side of Life

Be strong Mama, I have tried not to give-up…

Be brave as you have taught me to be

If I see you again, please don’t ask me what has happened to me.

If not mama, know that the worse is yet to happen because I choose not to give-up.

The stars will never shine bright again…

The moon will set at noon…

The cock will crow at Midnight…

It will never be the same again….

But I love you Mama!!!

...Dedicated to the abducted Chibok girls. #BringBackOurGirls