Sunday, June 2, 2013

What APC Must do: By Bashir Ahmad

1. The APC must translate its manifesto as many languages as possible.

2. The manifesto must be distributed across the entire country, not just within the zones that are APC strongholds, namely the North and Southwest.

3. The APC must immediately begin a registration process across the entire country.

4. The manifesto must ensure transparency in membership subscription in the political process of Nigeria.

5. The APC should reach out to the public to register as recorded members of the party.

6. It must ensure this registration is electronically recorded and publicized to encourage more Nigerians to join the cause.

7. It must generate revenue by charging a small fee for membership forms and demanding a donation from all its members. This way members will feel a part of the process and automatically expect nothing but transparency and inclusiveness in deciding the direction of the party.

8. The APC must ensure the process of internal democracy prevails, specifically enabling party members to vote and not just the leaders of the party or its delegates.

9. The APC must promise to do away with the habit of imposing candidates against the will of its party members and the Nigerian people.

10. It must respect the electoral process of the party and candidates must accept losses, by promising to unite behind the victorious candidate against the opposition.

11. It must encourage its prospective candidates to campaign on ideas and not violence or money politics.

12. The APC should continue to raise money by engaging its members in the development of the party.

13. The APC must create a culture where party members consistently donate to its treasury, no matter how small the sum is.

14. The APC should organize events and initiative to celebrate and appreciate the support of its dedicated members.

15. The party must work to involve the over 70% of Nigerians under the age of 40. And a first step is to appoint a National Youth Leader that was not alive during the Nigerian civil war, and have a strong social media presence.

From: @BashirAhmaad (bashahmad29@yahoo.com) +234(0)8032493020

Friday, May 31, 2013

NEMAN SHAWARA: NI DA MATAR ABOKINA

Ni da babban abokina mun kasance masu sharholiya da 'yan mata a lokacin da muke kan samartakarmu, amma cikin rahmar Allah, daga baya Allah ya shiryemu. Har Abokina ya samu budurwar da zai aura. Soyayyar ta su ba ta dau lokaci ba suka daidaita suka yi aure.

Wata rana bayan 'yan watanni da daura musu aure, mu kayi alkawarin zamu kai ziyara Bauchi, abokin nawa yace min na shirya da safe misalin karfe 9:00am nazo gidan shi don a motarsa zamu tafi, nace masa to Allah ya kaimu. Tun 8:30am naje gidansa, nayi packing motata, sannan na karasa cikin gidan, da na shiga sai Matar shi tace min ''Ai kuwa abokin naka yace idan kazo na sanar dakai cewar maganar tafiyarku ba zata yiwu ba, don an kirashi a gurin aiki emergency, don haka yace saidai ku sake saka wata ranar'' Sai nace to ai ba komai, amma mai yasa bai kirani a waya ya sanar dani ba?'' sai tace itama bata san dalili ba. Har na Juya zan fita sai tace ''Bashir dama ina da maganar da nake son yi da kai'' sai na juyo nace wace maganace haka? sai tace '' Bashir kaima kasan cewar Tun lokacin da abokika yake neman aure na, idan ya min laifi kai nake gayawa'' nace kwarai kuwa, to yanzu laifin mai ya miki?'' sai tace '' Ni gaskiya bazan boye maka ba, Abokinka baya gamsar dani wajen kwanciyar Aure'' Da naji haka sai maganar ta daure min kai, kafin nace kamai sai taci gaba dacewa '' Gaskiya Bashir kai kam duk matar da ta aureka zata More'' sai nace ban gane mai kike nufi ba'' sai tace '' Gaskiya da alama zaka iya gamsar da dukkan 'ya mace, Gaskiya da zaka aminci da ka biya min bukata ta ko sau daya ne''.

Tana fadan haka sai naji maganar ta kona min rai, kawai sai na hauta da fada da masifa, ina cewa '' Amma kin bani kunya, Ban taba tunanin zaki iya furta irin wannan kazamar maganar ba, ina daukar ki mai hankali ashe ba haka bane, yanzu kina nufin inci amanar abokina kenan?'' Da taga dai babu kofa sai tace ''Haba wallahi dama wasa nake maka, gwadaka kawai nakeyi'' sai nace mata ''To bari kiji na gaya miki, daga yau sai yau karki kara min irin wannan wasan'' sai na dauki hanya na fita.

Mai gadin gidan ya bude min Gate, zan fita kenan da motata sai ga Abokina shima ya nufo da motarshi sai nayi packing, shima ya tsaya, na fito daga motata nazo gurinshi, sai nace masa ''Ance min kaje aiki'' sai yace eh wallahi wani dan aikine ya taso mana a gurin aiki amma har na gama, yanzu sai ka shigo ka packing motarka a ciki sai mu tafi a tawa. sai na shigar da mota ta na ajiye. sannan na shiga tashi motar na zauna ina jiranshi ya shiga gida yayi sallama da matarshi. sannan ya fito muka tafi.

Tun wannan lokacin nake ta tunanin anya da gaske take cewar gwadani takeyi? Anya kuwa idan ta samu dama ba zata ha'inci abokina ba?

Ina neman shawararku shin ya kamata na sanar da abokina irin matar da yake zaune da ita? ko kuna ganin na rufa mata asiri?

NT: Abin lura duk da cewar wannan labari gaskiya ne amma ba da ni BASHIR din ya faru ba.

Follow me on Twitter @BashirAhmaad

Bazazzage Da Surukarsa Bakanuwa


Wani Bazazzage ne ya auri uwar gidansa Bakanuwa, wata rana ya raka ta ganin gida, sai aka kawo musu abinci irin na Kanawa hade da naman kaji, gogan naku saboda kunyar gidan surukai sai ya koshi, akai akai dashi yaci yace a'a. Nan aka ci gaba da hira da sirikarsa da matarsa da sauran mutanen gida, sai katsam aka dauke wuta, nan fa Bazazzage yaga duhu sai yasa hannu ya dauki cinya yana ci yana baza ido, ba za to ba tsammani kwatsam sai aka dawo da wuta. Sai gashi Bazazzage tsuru yana fisgar nama, nan fa kunya ta kama shi sai kawai ya fara kiran mis! mis!! mis!!! Hahahahahahahahaha!!!! Na sadaukar da wannan labari ga manyan dogarawa na Aliyu Danlabaran Zaria da Bashir Mukhtar Yusuf Zaria

Monday, March 11, 2013

Hoton Buhari Lokacin Yakin Neman Zaben 2011

General Muhammad Buhari lokacin yakin neman zabe a shekarar 2011.

Wannan hoto an samo shi ne a shafin yanar gizo na yakin neman Gen. Buhari.