Wannan Dandali Matattarar Tunani na ce, wato inda nake Bayyana ra'ayina game da al'amura daban - daban dake faruwa a harkokin rayuwarmu ta yau da kullum. Musamman akan siyasar Kasarmu Nigeria, nahiyarmu Africa, wani lokacin ma da duniya baki daya. Allah yayi mana Jagora!
Tuesday, January 15, 2013
Dariya: Tafiya Daga Kano Zuwa Lagos
Thursday, December 20, 2012
Budadden Sako Zuwa Ga Sabon Gwamnan Jihar Kaduna
Zuwa ga Mai Girma, Alhaji Mukhtar Ramalan Yero, Gwamnan Jihar Kaduna.
Assalamu – Alaikum!
Da farko ina yin mana jaje na rashin Gwamnanmu da mukayi Mr. Patrick Ibrahim Yakawo, a sanadiyar hadarin jirgin sama, muna fatan Allah Yasa ya taradda da yan’uwansa acan, mu kuma Allah Ya kyautata namu bayan nasu Yasa mu cika dakyau da Imani, ba yanda za ayi domin dukkan mai rai mai mutuwa ne.
Bayan haka, inaso in yi anfani da wannan dama domin inyi maka nasiha da kuma bada shawara, kasancewar bani da wata hanya da zanzo in sameka ni dakai sai ta wannan hanyar wanda na tabbata, in baka gani ba, wadanda suke kusa dakai zasu gani kuma zasu sanar dakai.
1. Da farko ina tunatar dakai da kara sanya jin tsoron Allah a cikin al’amuranka duka na yau da kullun, domin shi ne zai zame maka jagora akan dukkan abin da ka fuskanta.
2. Ka godewa Allah a bisa wannan ni’ima da ya yi maka. Ta yaya zaka gode maSa? Shi ne ta hanyar aikata abin da duk Ya umurce ka dasu gwargwadon ikonka, ka kuma nisanci duka abubuwan da Ya hanaka, idan ka siffantu da haka, to, shi zaisa Ya yi maka kari a bisa wannan ni’iman da Yayi maka yanzu.
3. Ka zamo mai adalci a bisa wadanda Allah Ya daura maka alhakinsu a kanka. Duk mai hakki ka bashi hakkinsa gwargwadon yanda doka ta tsara.
4. Ka zamo mai gaskiya da rikon amana da kuma daukan alkawarin abubuwan da kasan bisa ikon Allah bai fi karfinka ba.
5. Ka guji yin duka wani abu da zai zamo nau’in yin zalunci ne ga wadanda kake shugabanta, domin babu shamaki tsakanin addua’an wanda aka zalunta da Mahaliccinsa, kamar yanda Manzon Allah Sallallahu Alayhi Wasallam ya sanar damu haka, ya kuma ja kunnen mu akai.
6. Ni a tawa shawaran, ina ganin akwai wasu abubuwan guda biyu da suke neman sufi karfin talaka gabaki daya, wato sune harkan ilmi da abin da ya shafi harkan lafiya, ka sanya ido kai tare da bada dukkan gudummuwan da zaka iya badawa.
7. Ka sakamma kananan hukumomi mara domin suma su sami daman yin ma nasu al’ummomin ayyukan morewa. Ka kuma sanya ido akan yanda suke gudanar da harkokinsu gudun kada su wuce gona da iri.
8. Kula da harkan tsaro shima yana da matukar muhimmanci, domin sai da zaman lafiya ake samun daman gabatar da duk wasu ayyuka.
Daga karke, ina rokon Allah da Yayi maka jagora, Ya sanya maka hannu a bisa wannan nauyi da ya daura maka, Ya kasance tare dakai a duk inda kake, Ya baka ikon sauke dukkan nauyin da Ya daura maka, Ya kuma sanya maka katangar karfe tsakaninka da dukkan makiya mutun ko aljan. Muma Allah Ya biya mana dukkan bukatummu.
Wassalamu Alaykum,
ABDULKARIM MUH’D TANKO
Tuesday, November 13, 2012
Kotu Ta Yanke Wa Jarimi Sani Musa Danja Hukunci Daurin Shekara Guda A Gidan Yari
Kotun tafi da gidanka ta Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta yankewa shahararren dan wasan kwaikwayon nan na Hausa Sani Musa Danja daurin shekara guda a gidan yari.
Kotun ta daure Sani Danja ne sakamakon fitar da wani fim din sa mai suna Gudaliya ba tare da bin dokar hukumar tace finafinan ta jihar Kano ba, wanda hakan ya sabawa dokar hukumar ta sashi na 100 (2) ta shekarar 2001, sannan hukuncin da aka yanke masa na karkashin sashi na 112 na kundin tsarin mulkin hukumar.
Bayan samun sa da laifin, alkalin kotun mai shari'a Mukhtar Ahmad ya yanke wa Sani Musa Danja hukuncin zaman yari na tsawon shekara guda ko kuma biyan tarar N30,000, karkashin sashi na 157 na kundin hukunta masu laifuka, na shekara ta 2001.
Kotun ta daure Sani Danja ne sakamakon fitar da wani fim din sa mai suna Gudaliya ba tare da bin dokar hukumar tace finafinan ta jihar Kano ba, wanda hakan ya sabawa dokar hukumar ta sashi na 100 (2) ta shekarar 2001, sannan hukuncin da aka yanke masa na karkashin sashi na 112 na kundin tsarin mulkin hukumar.
Bayan samun sa da laifin, alkalin kotun mai shari'a Mukhtar Ahmad ya yanke wa Sani Musa Danja hukuncin zaman yari na tsawon shekara guda ko kuma biyan tarar N30,000, karkashin sashi na 157 na kundin hukunta masu laifuka, na shekara ta 2001.
Yan Fashi Sun Kai Farmaki Kasuwar Chanji ta Wapa a Jihar Kano
Da tsakar ranar Talatar nan ne wasu yan fashi da makami suka kai farmaki kasuwar yan chanji dake Wapa a birnin Kano. Yan fashin su kimanin 9 da suke akan babura da kuma mota kirar Golf sun ringa harbi babu kakkautawa a kasuwar daga bisani suka kutsa cikin wani shago suka yi awon gaba da miliyoyin kudi da har yanzu ba a tantance yawansu ba.
Shugaban kasuwar Wapa Alhaji Auwal Umar Nagari ya bayyana takaici bisa rashin isowar jami'an tsaro akan lokaci da kuma yadda yan fashin suka bar wasu kwanson harsasai mai dauke da tambarin 'yan sanda lamarin da yasa suke zargin kodai akwai lauje cikin nadi. yawan fashi a kasuwannin jihar Kano dai wani babban al amari ne da a yanzu ke nema zama ruwan duk da yawan jami'an tsaro dake baje a hanyoyin jihar.
Freedom Radio FM, Kano
Shugaban kasuwar Wapa Alhaji Auwal Umar Nagari ya bayyana takaici bisa rashin isowar jami'an tsaro akan lokaci da kuma yadda yan fashin suka bar wasu kwanson harsasai mai dauke da tambarin 'yan sanda lamarin da yasa suke zargin kodai akwai lauje cikin nadi. yawan fashi a kasuwannin jihar Kano dai wani babban al amari ne da a yanzu ke nema zama ruwan duk da yawan jami'an tsaro dake baje a hanyoyin jihar.
Freedom Radio FM, Kano
Kano tribunal jails Sani Danja
Kano State Censorship Tribunal sitting has sentenced popular Hausa film actor, Sani Musa Danja to one year imprisonment.Sani Danja was sentenced yesterday for exhibiting for sale an uncensored and unlicensed copy of a film titled “Gudaliya” in contravention of Section 100 (2) of the state Cinematography Censorship Regulation 2001 and punishable under Section 112 of the same law.
He pleaded guilty and asked the court for leniency. Senior State Counsel Hussain Hassan therefore applied for summary trial under section 157 of the criminal procedure court. Chief Magistrate Mukhtar Ahmed sentenced him to one year imprisonment or to pay a fine of N30,000.
Culled: Daily Trust
He pleaded guilty and asked the court for leniency. Senior State Counsel Hussain Hassan therefore applied for summary trial under section 157 of the criminal procedure court. Chief Magistrate Mukhtar Ahmed sentenced him to one year imprisonment or to pay a fine of N30,000.
Culled: Daily Trust
Subscribe to:
Posts (Atom)

