Friday, May 28, 2010

RIBA KO HASARA

29th May 1999 daga wannan rana zuwa yau shekaru goma sha daya kenan kuma adadin shekarun da kasar Nigeria ta canja tsarin mulkin kasar zuwa tsari democradiya, irin tsarin da kasar America ke amfani dashi.

Cikin wannan shekaru Nigeria tayi shugabanni guda uku biyu daga kudu, daya daga arewa. Biyu daga ciki zaben su muka yi daya kuma ya samu mulkin ne a matsayin na mataimaki bayan shugaban daya ke kai Allah yayi mai rasuwa.

Nigeria kasa ce wadda Allah ya albarkan ce ta da arzukin noma, ma'adanan kasa da kuma man futar, wannan dalili yasa ake ganin duk nahiyar Africa ba wata kasa da takaita arzuki. Ga kuma yawan jama'a da Allah ya hore mata sama da mutum miliyan dari da talatin, 130,000000.

Amma kash duk da irin wannan abubuwa da Allah ya hore mana bamu samu shugabanni nagari ba. Sai dai muna adu'ar Allah ya albarkan ce mu da shugabanni nagari.

Tambaya anan wai shin a wannan tsarin da kasar mu ta zaba na democradiya ta koma. Shin Riba aka ci ko Hasara aka yi.

A karshe ina taya dukkan daukakin al'ummar kasar Nigeria da kuma dukkan masoyanta kasar Murnar zagayowar wannan rana ta demokradiya wato Democracy Day

Thursday, May 13, 2010

BRAZIL BATA GAYYACI MANYAN YAN WASA BA


Brazil ta sanar da sunayen yan wasa 23 wadanda zasu buga mata wasa a gasar cin kofin duniya da za'a buga a kasar South Africa a wata mai zuwa. Abin mamaki shine Brazil bata gayyaci shahararrun yan wasanta ba, kamar su: Ronaldo, Roberto Carlos, Ronaldinho, Adriano, Alexandre Pato da kuma Neymar. Yan wasan da ake gani idan Brazil bata gayyace su ba. Ba abin azo a gani zatayi a gasar ba.

Brazil itace kasar da ta halacci dukkan gasar tunda aka fara, kuma itace wadda tafi kowace samun nasarar daukar kofin har sau biyar.

Brazil na rukunin H ne tare da kasashen Portugal, Ivory Coast da kuma South Korea.

Cikakken jerin yan wasa da aka gayyata:

MASU TSARON GIDA
Julio Cesar (Inter Milan ITA)
Doni (AS Roma ITA)
Gomes (Tottenham Hotspur ENG)

MASU BUGA BAYA
Maicon (Inter Milan ITA)
Daniel Alves (Barcelona ESP)
Michel Bastos (Lyon FRA)
Gilberto (Cruzeiro BRA)
Lucio (Inter Milan ITA)
Juan (AS Roma ITA)
Lusaio (Benfica POR)
Thiago Silva (AC Milan ITA)

MASU BUGA TSAKIYA
Gilberto Silva (Panathinaikos GRE)
Felipe Melo (Juventus ITA)
Ramires (Benfica POR)
Elano (Galatasaray TUR)
Kaka (Real Madrid ESP)
Julio Baptista (AS Roma ITA)
Kleberson (Flamengo BRA)
Josué (VfL Wolfsburg GER)

MASU BUGA GABA
Robinho (Santos BRA)
Luis Fabiano (Sevilla ESP)
Nilmar (Villar Real ESP)
Grafile (VfL Wolfsburg GER)

Sunday, May 9, 2010

GASAR FIFA WORLD CUP 2010


Gasar World Cup 2010 karo na 19th kuma za'a yi shine tsakanin 11 June da 11 July 2010 a kasar South Africa, kuma wannan gasa itace karon farko da za'a yi a nahiyar Africa. Bayan da hukumar FIFA ta maida tsarin gasar nahiya-nahiya.

South Africa ta samu nasarar daukar nauyin gasar ne bayan ta doke abokan takarar ta Morocco, Egypt, Libya da Sudan.

KASASHEN DA ZASU BUGA GASAR

Kasashe 32 ne zasu ta ka leda a wannan gasa daga bangare 6 na duniya, kasashen sune:-

AFC (4)
Australia
Japan
Korea DPR
Korea Republic

CAF (6)
Algeria
Cameroon
Cote d'Ivoire
Ghana
Nigeria
South Africa

CONCACAF (3)
Honduras
Mexico
United States

CONMEBOL (5)
Argentina
Brazil
Chile
Paraguay
Uruguay

OFC (1)
New Zealand

UEFA (13)
Denmark
England
France
Germany
Greece
Italy
Holland
Portugal
Slovenia
Slovakia
Spain
Switzerland

FILAYEN WASA

Za'a yi wannan gasa ne a filayen wasanni guda 12 kuma biyar da cikin su sabbi ne an gina sune domin wannan gasa ta FIFA World Cup 2010, filayen sune:-
Johannesburg (A) 94,700
Durban 70,000
Cape Town 69,070
Johannesburg (B) 62,567
Pretoria 51,760
Nelson Mandela 48,000
Bloemfontein 48,000
Polokwane 46,000
Rustenburg 44,530
Nelspruit 43,589

Kowacce kasa zata zo da yan wasa guda 23 kamar yadda akayi a gasar 2006 a kasar Germany. Kuma dole kowacce kasa ta sanar da sunayen yan wasanta ga hukumar FIFA kafin ranar 1 June 2010.